Damaturu | |||||
---|---|---|---|---|---|
| |||||
Wuri | |||||
| |||||
Ƴantacciyar ƙasa | Najeriya | ||||
Jiha | Jihar Yobe | ||||
Babban birnin | |||||
Yawan mutane | |||||
Faɗi | 88,014 lissafi | ||||
• Yawan mutane | 37.2 mazaunan/km² | ||||
Labarin ƙasa | |||||
Yawan fili | 2,366 km² | ||||
Altitude (en) | 371 m | ||||
Bayanan Tuntuɓa | |||||
Kasancewa a yanki na lokaci |
Damaturu ƙaramar hukuma ce kuma babban birnin jihar Yobe dake arewa maso gabashin Najeriya.[1] Nan ne hedikwata inda fadar gwamnatin Jihar Yobe take wadda gwamna Mai Mala Buni ke mulkinta a halin yanzu, sannan kuma cibiyar gudanar da mulki na jahar. Masarautar Damaturu, ita ce masarautar gargajiya daya jal ta sarkin yanka mai daraja ta ɗaya a gabadaya fadin birnin. Kebantacciyar lambar akwatin waya na birnin ita ce 620. Karamar hukumar tana da fadin kasa 2,366 2 da yawan jama'a 88,014 a ƙidayar shekara ta 2006. Garin Damaturu yana kan babbar hanyar A3. A alkaluman ilimin zanen kasa, birnin Damaturu ya gindayu ne akan alkaluman kwa'odineto 12°00′00″N 12°00′00″E / 12.00000°N 12.00000°E.
Damaturu ta kasance a matsayin mallaka a lokacin da turawan Ingila suka sassaka ta daga gundumar Alagarno . Hakan ya haifar da mamaye daular Bornu a shekara ta 1902 da sojojin mulkin mallaka karkashin jagorancin Kanar Thomas Morland suka yi.
Damaturu dai ya sha fuskantar hare-haren mayakan jihadi na Boko Haram a yakin da suke yi na kafa daular halifanci a yankin arewa maso gabas.
11°44′40″N 11°57′40″E / 11.74444°N 11.96111°EPage Module:Coordinates/styles.css has no content.11°44′40″N 11°57′40″E / 11.74444°N 11.96111°ESamfuri:Yobe State